Tashin hankali ba zai kawo ƙarshen matsalar ƙarancin kuɗi ba – Gwamnan Legas

Date:

Gwamnan jihar Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya Babajide Sanwo-Olu ya yi kira ga jama’ar jihar da su kwantar da hankulansu kan fusatar da suka yi dangane da wahalhalun ƙarancin kuɗi da ake fuskanta a ƙasar.

 

Gwamnan ya yi wannan kira ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a fadar gwamnatin jihar da ke Marina, kan matsalar da ake ciki ta sauyin kuɗi a ƙasar.

Talla

Sanwo-Olu ya umarci mazauna jihar da su kauce wa duk wani tashin hankali, da zanga-zanga da ƙone-ƙone yana mai cewa hakan ba zai kawo mafita ga matsala ko wahalhalun da ake ciki ba

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

Ya ce “Ina mai jinjina a gare ku mutanen Legas dangane da haƙuri da juriya da kuka nuna a cikin wannan hali da ake ciki na tsaka-mai-wuya”.

 

“yan uwana al’ummar Legas, ina kira da tattausar murya a gare ku, a matsayina na gwamnanku, dan Allah ku kwantar da hankula a wannan lokaci, ku guji duk wani abu da zai tayar da hankali da zanga-zanga da kuma ƙone-ƙonea faɗin jiharmu”, in ji gamnan.

 

“Duk da wahalhalun da kowa ke ciki, tashin hankali ba zai zame mana mafita ba, duka mun sani cewa akwai mutanen da ke son yin amfani da tashe-tashen hankulan ta hanyar yin kalaman da ke tunzura jama’a”

 

”Kuma duk suna yin wannan ne da nufin hana ku damar kaɗa ƙuri’unku a zaɓen shugaban ƙasa, ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki, dan haka kada ku ba su dama su cimma manufarsu,”in ji Sanwo-Olu.

 

gwamnan ya ci gaba da cewa ba adalci ba ne kai hari kan dukiyoyin gwamnati da na al’umma.

 

A ranar Juma’a ne dai aka samu rahotonnin da ke cewa wasu fusatatun matasa sun toshe wasu titunan birnin Legas tare da ƙona tayoyi, sakamakon fusatar da suka yi kan ƙarancin takardun naira a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...