Ina jan kunnen masu ‘yaɗa jita-jitar kafa gwamnatin riƙon kwarya a Najeriya – Buhari

Date:

Fadar shugaban ƙasar Najeriya ta ce babu ƙamshin gaskiya cikin kalaman da ake yaɗawa kan cewa Muhammadu Buhari na shirin miƙa mulki ga gwamnatin riƙon ƙwarya.

 

Cikin wata tattaunawa da ya yi da BBC, mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan lamuran yaɗa labarai Malam Garba Shehu ya ce, “ya kamata a daina ɗaukar lamarin gwamnatin riƙo da wasa, maganar zaɓe na nan daram.”

Talla

Yayin da aka jiyo wasu shugabannin na zargin cewa Shugaba Buhari na neman daƙile kafafun dimokradiyyar Najeriya, a wani gefen kuma iƙirari ne kan cewa ƙarancin naira da ake fama da shi a Najeriya wani ɓangare ne na janyo koma baya ga zaɓe mai zuwa da za a gabatar nan da kwanaki, da kuma shirin miƙa iko ga gwamnatin riƙo.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

A nasa martanin kakakin shugaban ƙasar ya ce wannan wani salo ne mai cike da haɗari da wasu mutane suka ɗauka waɗanda suke ganin za su iya faɗuwa zaɓen.

 

Ya ƙara da cewa ƙirƙiro yanayin da zai jefa mutane cikin firgici ba hanya ba ce da za ta kawo ƙarshen damuwar da aka shiga ba ta sauyin naira.

 

Yace sauyin kuɗin ba a ƙirƙiro shi ba ne domin ya bai wa shugaban ƙasa damar zama a kan karagar mulki har bayan 29 ga watan Mayu, yana cewa “fadar shugaban ƙasa a shirye take ta miƙa mulki ga duk wanda ya ci zaɓe domin gadar Shugaba Buhari.

 

Kuma za a yi hakan ne a ranar 29 ga watan Mayun 2023 kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...