Yanzu-Yanzu: Buhari ya Magantu kan halasci ko Haramcin tsofaffin kuɗin Nigeria

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da ikirarin cewa gwamnatin tarayya ko babban bankin Najeriya CBN sun ki amincewa da ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000 duk da hukuncin kotun koli.

 

Zamfara, Kaduna da Kogi sun garzaya kotun kolin Najeriya domin neman agaji a madadin al’umomim su domin kalubalantar wa’adin da babban bankin kasar CBN ya kakaba na rufe karbar tsofaffin takardun kudin naira a ranar 10 ga watan Fabrairu.

Talla

Kotun koli, a hukuncin da ta yanke a ranar 8 ga Fabrairu, ta umurci dukkan bangarorin da kada su ɗauki wani mataki tare da soke wa’adin 10 ga watan Fabrairu 10, har zuwa lokacin da za a yanke hukunci kan karar da aka dage sauraron ta zuwa ranar 15 ga Fabrairu, 2023.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Sai dai kuma cibiyoyin hada-hadar kudi da su ka hada da bankuna da gidajen mai da manyan kantuna da sauran ‘yan kasuwa na ci gaba da kin karɓar tsoffin takardun Naira duk da hukuncin da kotun koli ta yanke.

An ruwaito cewa wasu bankunan sun dogara ne da cewa CBN ya aika musu da umarni a wata takarda.

An kuma ambato gwamnan babban bankin na CBN a wani taro da jami’an diflomasiyya a jiya Talata a Abuja yana cewa daga ranar 10 ga Febrairu tsofaffin takardun kudi za su daina aiki.

Sai dai kuma Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasa, a daren ranar Talata a wata sanarwa, ya ce:

“Muna so mu bayyana cewa ba gaskiya ba ne gwamnatin tarayya ko babban bankin Najeriya, CBN sun dauki mataki kan halascin kudade za su ci gaba da aiki duba da yadda shari’ar ta ke gaban kotun koli.

“Za a sanar da matsayar gwamnati da na CBN bayan an yanke hukuncin gobe.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...