Za mu kwace lasisin wurin kasuwancin duk masu kin karɓar tsofaffin kudi a Kano – Ganduje

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
 Gwamnatin jihar Kano ta yi gargadin cewa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen soke lasisin gudanar da harkokin kasuwanci na manyan ‘yan kasuwa ko kuma daukar mataki kan duk wanda ya ki karban tsofaffin kuɗi idan an zo sayan kayansu.
Kadaura24 ta rawaito Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ne ya yi gargadin a wata

Talla

sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar, ya ce har yanzu doka bata hana karbar tsofaffin kudi ba.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Ya ce kotun koli ta jaddada hukuncin wucin gadi da ta yi kan batun tsofaffin takardun kudin, Inda ta bada umarnin a ci gaba da yin amfani da su tsofaffin kudin tare da Sabbin har sai ta yanke hukunci akai.
 Gwamnan yace gwamnati ta Sami labarin cewa wasu ‘yan kasuwa kamar manyan kantuna, kantuna, bankuna, gidajen cin abinci, otal-otal, ‘yan kasuwa a kasuwanni, gidajen mai, wuraren ajiye motoci, da dai sauransu, suna da kin karɓar tsohon kudin wanda kuma hakan ba dai-dai .
 Ganduje ya kuma kara da cewa rashin karbuwar kudin da wasu marasa kishi suke yi, na dagula al’amura da dama.
 Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu na yau da kullum tare da kai rahoton duk wanda ya ki karban tsohuwar takardar naira zuwa ga hukuma mafi kusa domin daukar mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...