Muna kira ga Gwamnatin Najeriya da ta binciki kisan Gillar da aka yiwa yan Tijjaniyya – Dan Almajiri

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Anyi kira ga Gwamnatin Najeriya ta binciki zargin kisan gilla da wasu mutane dake sanye da kayan Sojoji a Kasar Burkinafaso suka yiwa wasu yan Najeriya 17 da suke kan hanyarsu ta zuwa Kasar Senigal domin halartar Mauludin Shehu Ibrahim Inyass.

 

Kadaura24 ta rawaito annan kira na kunshe ne cikin wata sanarwar Ta’aziyya da Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa ta fitar mai dauke dasa hannun shugaban Kungiyar Barista Habibu Dan Almajiri da Babban Sakataren Kungiyar Shehu Tasiu Ishaq.

 

Mutanen dai suna kan hanyarsu ne ta zuwa garin Kaulaha dake kasar Senigal a motoci wadanda suka tashi daga nan Najeriya domin halartar Mauludin Shehu Ibrahim Inyass, kamar yadda aka saba gabatarwa duk shekara a can garin Madinatu Kaulaha.

 

Yayin da ake zargin Sojojin Kasar Burkinafaso, sun bude musu wuta bayan sun tsayar da motocinsu kuma suka harbesu har lahira.

Talla
 
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Daganan sanarwar tayi addu’ar Allah ya jikansu kuma ya karbi shahadarsu yakai rahama kabarinsu ya bawa iyalansu hakurin jure rashinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...