Karancin Man Fetur ka iya shafar zabe a Nigeria – INEC

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC ta ce matsalar ƙaramncin man fetur da ƙasar ke fuskanta ka iya shafar tsare-tsaren hukumar game da za ta shirya zaɓen ƙasar da ke tafe.

Shugaban Hukumar Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Talata a Abuja a lokacin taron tuntuɓa tsakanin hukumar da ƙungiyoyin direbobin haya na ƙasar waɗanda suka haɗar da NARTO da NURTW da sauransu.

“Hukumar zaɓe tana tare da ku game da kokenku na ƙarancin man fetur da ƙasar nan ke fuskanta, da yadda hakan zai shafi hakar sufuri musamman a ranar zaɓe,” in ji Mahmood.

Ya ƙara da cewa “magana ta gaskiya ita ce rashin wadataccen man zai shafi shirye-shiryenmu”. Inji Farfesa Mahmoud

Talla

Shugaban hukumar ya ce dangane da wannan dalili , hukumar zaɓe za ta gana da kamfanin mai na ƙasa NNPCL domin duba hanyoyin da ya kamata a bi wajen magance wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...