Allah ya yi wa Sarkin Dutse, Nuhu Muhammad Sunusi rasuwa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Allah ya yi wa Sarkin Dutse, Nuhu Muhammad Sunusi rasuwa.

Kwamishinan ayyuka na musamman a Jihar Jigawa Auwal Danladi Sankara ne ya tabbatar wa BBC da rasuwar sarkin.

Sarkin ya rasu ne ranar Talata a Abuja bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya kuma ya rasu yana da shekara 79.

Sakatare na musamman na marigayin Wada Alhaji Dutse ya tabbatar wa BBC cewa ana sa ran yin jana’izar sarkin ne a ranar Laraba a Dutse.

Kafin rasuwarsa, sarkin ya taɓa zama Uban Jam’iar Jihar Sokoto wato Sokoto State University.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...