Buhari ya dage sai ya zo Kano, duk da shawarar Ganduje

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Duk da dakatar da ziyararsa da Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya yi, akwai yiwuwar Shugaban Ƙasa, Muhammadu ya, zai ziyarci jihar gobe Litinin kamar yadda aka tsara.

 

Wani bincike ya nuna cewa Shugaba Buhari bai gamsu da dalilin da gwamnatin jihar Kano ta bayar na dakatar da ziyara tasa ba.

 

A wani taro da ya yi da masu ruwa da tsaki a gidan gwamnatin jiha, Gwamna Ganduje ya shawarci Shugaba Buhari da ya dakatar da ziyarar, duba da wasu dalilai .

Talla

A wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamna Malam Abba Anwar ya aikowa kadaura24 yace matakin da gwamnatin kano ta dauka ya sami goyon bayan dukkanin masu ruwa da tsaki a kano.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Jaridar Sunday Tribune ta gano cewa Shugaba Buhari ya dage cewa shi fa ba abin da zai hana shi kawo wannan ziyara.

A gobe Litinin ne dai ake sa ran Buhari zai shigo Kano domin bude tashar tsandauri ta Dala, wadda gwamnatin tarayya ta samar karkashin jagorancin sa kamar yadda ake ta sanarwa a kafafen yada labarai.

Banda ayyukan da gwamnatin jihar Kano ta gudanar, akwai wasu ayyuka da gwamnatin tarayya ta gudanar waɗanda aka tsara Shugaba Buhari zai ƙaddamar.

 

Shugaban ya yanke shawarar cewa zai zo Kano don ƙaddamar da ayyukan na gwamnatin tarayya.

 

Tuni tawagar Shugaban Ƙasar ta dira a Kano, kuma har zuwa ranar Asabar da daddare ba a ce su bar Kano zuwa Abuja ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...