Wahalar mai da sauyin kudade makarkashiya ce don kar naci zabe – Tinubu ya koka

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya bayyana wahalar man fetur da ake fuskanta da kuma batun sauyin kudade da cewa makarkashiya ce ake yiwa jam’iyyar APC don kar taci zaben mai zuwa.

Talla

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a Abeokuta, jihar Ogun, yayin yakin neman zabensa.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

 

Yace bai adace a irin wannan lokaci a fito da manufofin da zasu wahalar da al’umma ba kuma har ma su hana su fito domin kada kuri’a a zaben watan gobe dake tafe.

 

Ya ce zabukan da ke tafe za su kasance mafi girman juyin juya hali.

 

“Ba sa son a gudanar da wannan zabe.

 

Suna son yi mana zagon kasa a zaben.

 

Shin za ku kyale su”,

 

Tinubu ya tambayi magoya bayan da suka hallara a wurin taron, inda suka amsa da “A’a.”

 

Tinubu ya sha alwashin cewa “za mu yi amfani da PVC mu karbe gwamnati daga hannunsu,” kamar yadda ya nuna cewa zabe mai zuwa zai zama “juyin juya hali.”

 

“Ko da sun ce babu mai, za mu yi tattaki don kada kuri’a.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...