Masari ya fitar da Naira Miliyan 500 ga kananan hukumomin Katsina don tara Jama’a saboda zuwan Buhari

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya amince a fitar da Naira miliyan 500 ga daukacin kananan hukumomin jihar 34 domin tara Jama’ar jihar sakamakon ziyarar aiki ta kwanaki biyu da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kai jihar a watan Janairu. 26 da 27.
 Jaridar Solace Base ta Sami tabbacin hakan ne cikin wata wasika dake dauke da amincewar gwamna Masari , inda ta bayar da izinin sakin “N14,695,588.00 ga dukkanin kananan hukumomin guda 34 da ya kai N499,650,000.00 (Miliyan dari hudu da casa’in da tara, Naira dubu dari shida da hamsin kacal). Kuma wadannan kudaden an fitar da su ne daga asusun hada ka na kananan hukumomi 34 da ke jihar don fito da al’ummar jihar domin su tarbi Shugaban kasa a ziyarar aiki da zai kai jihar Katsina daga ranar 26-27 ga Janairu, 2023.
 Yahuza S. Ibrahim, ne yasa hannu a wasikar a madadin babban sakataren gidan gwamnatin jihar Katsina da kuma aka turawa kwamishinan kananan hukumomi da masarautu n jihar.
Talla
 A cikin kwafin wasikar da kadaura24 ta gani an tura wasikar zuwa ofishin babban akanta janar na jihar, ma’aikatar kudi da kuma babban mai binciken kudi domin gaggauta biyan kudin kafin zuwan Muhammadu Buhari kafin ranar 26 ga watan Janairu.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Jihar Katsina dai kusan kashi 70 cikin 100 na mazauna jihar na fama da talauci, kamar yadda wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar a watan Satumban da ya gabata, wasu da dama na ganin magudan kudaden da aka fitar kawai don tarbar shugaban kasar almubazzaranci ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...