Bana goyon bayan matakin da CBN ta dauka akan sauyin kudade – Sanata Kabiru Gaya

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Sanatan kano ta Kudu Kabiru Ibrahim Gaya ya ƙalubalanci rashin Kara wa’adi da tsoffin kuɗade a Nigeria, sakamakon mawuyacin halin da al’umma suka shiga.

“Wannan tsarin bama goyon bayan sa saboda babu sauki a cikin sa, babban abun jin tausayin ma shi ne mutanen mu na karkara saboda su ne suke da karamin karfi kuma basu da masaniyar yadda zasu Kai kudaden su banki”. Inji Sanata Gaya
Kadaura24 ta rawaito Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai.
Talla
Yace a matsayin su na ‘yan majalisa sun yi iya bakin kokarin su don ganin an kara wa’adin karbar tsofaffin kuɗin domin a saukaka talakawa Masu karamin karfi.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
  • “Ana cewa wai saboda yan siyasa aka dau wanann mataki, Amma ya kamata a sani yan siyasa masu takara tun watanni uku da suka gabata suka tanadi abun da suke bukata, akwai talakawa ne zasu sha wahala”. Inji Gaya
Sanata Kabiru Gaya ya kara da cewa yana kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya gaggauta umartar gwamnan babban bankin kasa daya Kara wa’adin karbar tsofaffin kuɗin ko dan a saukakawa kananan yan kasuwa da talakawa.
” Kamata yayi abi a hankali wajen janye tsaffin kuɗin har sai sabbin kudaden da aka saura fasalinsu wadata, amma wannan tsarin gaskiya akwai matsala sosai , kuma wani zalunci da ake shi ne Kaba da Naira dubu 20 tsofaffi a baka Naira dubu 10 Sabbin wannan zalunci ne”. A cewar Sanata Gaya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...