Rikicin Siyasa a Kano rashin daukar mataki daga yan Sandan ke kara haifar da shi – Abba Gida-gida

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Dan takarar gwamnan jihar Kano a tutar jam’iyyar NNPP a zaben shekara ta 2023 Engr. Abba Kabir Yusuf ya ce ‘yan sanda ne basa daukar mataki shiya rikice-rikicen siyasa ke karuwa.

 

Abba K Yusuf wanda ake yiwa lakabi da Abba Gida-gida ya bayyana hakan ne a ranar Talata a wajen taron zaman lafiya na Kano wanda rundunar ‘yan sandan jihar tare da hadin gwiwar AMG Foundation da sauran kungiyoyin farar hula a karkashin G31 suka shirya.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanya wa hannu kuma ya aikowa kadaura24, Abba Gida Gida ya ce jam’iyyun adawa a Kano sun hada kai kan duk wani nau’i na barazana da batanci daga jam’iyyar APC mai mulki, yana mai bayanin cewa tana amfani da damar ta wajen cin zarafin wasu zababbun al’umma.

Talla

 

A cewar sanarwar, dan takarar gwamnan ya tuna yadda aka far mu su da ake zargin shugaban jam’iyyar APC na jihar Abdullahi Abbas da dansa Sani Abdullahi Abbas AKA (Ochi) ne suka shirya su.

 

“Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP ya ci gaba da ba da shawarar cewa, muddin ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro ba su gudanar aiyukan su yadda doka ta tanada dan cika alkwarin da suka dauka na kama aiki.

 

A karshe sanarwar ta ce matukar hakan ta gagara to wajibi ne abar al’ummar jahar Kano su kare kansu kamar yadda doka ta bada dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...