Ku yada zaman lafiya da hadin kan Kasa – Shugabar NYSC ta buƙaci Matasan

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Mukaddashin Darakta-Janar ta hukumar kula da masu yi wa kasa hidima (NYSC), Misis Christy Uba, ta yi kira ga ‘yan yiwa kasa hidima dasu kasance masu yada zaman lafiya don samar da hadin kan kasa a lokaci da kuma bayan kammala aikin su na yiwa kasa hidima.

 

 

Christy Uba ta yi kiran ne a yayin bikin rantsar da rukuni ‘C’ kashi na 2 na shekarar 2022 na yan yiwa kasa hidima, wanda ya gudana a sansanin NYSC dake Kusalla a karamar hukumar Karaye a jihar Kano.

 

Shugabar hukumar wadda ta samu wakilcin shugabar hukumar NYSC ta jihai kano, Hajiya A’isha Tata Muhammad, ta bukaci ‘yan NYSC din da su nuna matukar da’a da kuma inganta hadin kan kasa.

 

 

Ta kara musu kwarin gwuiwa da su yi amfani da damar da aka basu,  wajen koyon sana’o’in dogaro da kai da za’a koya musu, a yayin zaman da zasu yi na tsawon makonni uku a sansanin.

Talla

 

Uwargida Uba ta bukaci masu yiwa kasa hidima da su guji amfani da kafafen sada zumunta wajen yada labaran karya, da rura wutar kiyayya da sauran munanan aiyuka, maimakon haka su samar da wata hanya guda domin bunkasa hadin kan kasa da ci gaban kasa.

 

A nata jawabin, kodinetar shirin ta kano na jiha Hajiya Aisha Tata Mohammad wadda Daraktan sansanin Alhaji Bala Dabo ya wakilta ta ce an tsara shirin ne domin baiwa masu yiwa kasa hidimar gudanar da aikin hidimar kasa na shekara guda tare da koya musu darussa da sana’o’i kala-kala.

 

Ko’odinetan ta ci gaba da cewa an kimanin matasa 1,136 aka yiwa rajista a sansanin wanda 542 daga cikinsu maza ne da Kuma mata 594.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...