Zan Magance Matsalolin Makarantar Firamare ta unguwa uku nan bada jimawa ba – Dan Majalisar Tarauni

Date:

Daga Auwalu Shugaba U/uku

 

Dan majalisar dokokin jihar kano mai wakiltar karamar hukumar Tarauni Hon. Lawan Rabi’u Journalist, ya bada tabbacin tallafawa makarantar gidan gona special primary school unguwa uku, don inganta harkokin koyo da koyarwa a makarantar.

” Insha Allah zan yi iya bakin gwargwadon ikona, inga matsalolin da suke damun wannan makaranta na kawar da su kona share muku hawaye insha Allahu rabbi”. Inji Lawan Rabi’u
Talla
Lawan journalist ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar wadda yanzu aka fi sani da unguwa uku special primary school.
” A zahirin gaskiya naji dadin wannan ziyara kuma ta tunamin abubuwa da dama da na ga wadannan fuskokin, kuma na dada sanya kishin wannan makarantar a cikin zuciya ta” . Inji Dan majalisar
Da yake bayyana makasudin ziyarar tasu Shugaban kungiyar Malam Adamu Jafar yace sun ziyarci dan majalisar ne domin su yi masa fatan alkhairi kasancewar sa Dan kungiyar Kuma tsohon dalibin makarantar, Sanna su sada zumuncin da aka kafa kungiyar domin sa.
Yace sun sanar da shi tarin matsalolin da suka da baibaye makarantar domin ya taimaka ya magance wasu daga cikin matsalolin ko a kara inganta harkokin koyo da koyarwa a makarantar, kasancewar makarantar tana da dalibai masu tarin yawa.
Malam Habibu Abdullahi shi ne shugaban makaranta ta unguwa uku special primary school yace makarantar tana fama da matsalolin da suka hadar da karancin kujerun zama na dalibai kayan koyo da koyarwa da dai sauransu .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...