Daga Auwal Alhassan Kademi
Matuka baburan adaidaita sahu a jihar kano su bi dokar da gwamnatin jihar kano ta dora musu ta hana su bin wasu manyan titunan jihar.
Kadaura24 ta rawaito tun daren litinin din data gabata ne gwamnatin jihar kano ta karkashin hukumar Karota ta bada sanarwar dakatar da yan adaidaita sahun daga bin wasu manyan tituna a Kano.

Binciken da jaridar kadaura24 ta gudanar ya nuna cewa yan adaidaita sahun sun bi waccen doka, domin kuwa sun ƙauracewa titunan da aka ce ba’a son ganin su akai, wadanda suka hadar da tituna Ahmad Bello way by Mundubawa da Kuma tal’udu zuwa gwarzo.

Wakilin mu ya shaida yadda aka jibge jami’an hukumar karota domin ganin sun tabbatar da ba Wani dan adaidaita sahu da ya karya dokar.
Gwamnatin kano dai tuni ta samar da manyan motocin safa-safa domin maye gurbin yan adaidaita sahun da su a kokarin ta na Kara inganta harkokin sufuri a kano, haka Kuma gwamnatin ta yi alkawarin karo wasu motocin domin sanyasu a sauran manyan titunan jihar kano.

