Shin Yan adaidaita sahu sun bi sabuwar dokar hana su hawa manyan titunan Kano kuwa ? 

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi
Matuka baburan adaidaita sahu a jihar kano su bi dokar da gwamnatin jihar kano ta dora musu ta hana su bin wasu manyan titunan jihar.
Kadaura24 ta rawaito tun daren litinin din data gabata ne gwamnatin jihar kano ta karkashin hukumar Karota ta bada sanarwar dakatar da yan adaidaita sahun daga bin wasu manyan tituna a Kano.
Talla
Binciken da jaridar kadaura24 ta gudanar ya nuna cewa yan adaidaita sahun sun bi waccen doka, domin kuwa sun ƙauracewa titunan da aka ce ba’a son ganin su akai, wadanda suka hadar da tituna Ahmad Bello way by Mundubawa da Kuma tal’udu zuwa gwarzo.
Wakilin mu ya shaida yadda aka jibge jami’an hukumar karota domin ganin sun tabbatar da ba Wani dan adaidaita sahu da ya karya dokar.
Gwamnatin kano dai tuni ta samar da manyan motocin safa-safa domin maye gurbin yan adaidaita sahun da su a kokarin ta na Kara inganta harkokin sufuri a kano, haka Kuma gwamnatin ta yi alkawarin karo wasu motocin domin sanyasu a sauran manyan titunan jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...