Mamallakan jiragen kansu a Najeriya sun maka gwamnati kotu

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

Masu jiragen sama na kashin kansu a Najeriya sun yanko wa gwamnati sammaci, inda su ke bukatar kotu ta hana ta dakatar da jiragen nasu tashi saboda kin biyan kudin fito.

A watan Nuwamban bara ne hukumar hana fasa kwauri ta kulle jirage 91 mallakar wasu hamshakan masu arziki a kasar, bisa zargin kin biyan kudaden fito da yawansu ya haura naira biliyan 30.

Talla

Hukumar ta kwastam ta samu sahalewa daga ofishin Shugaban kasa, na umurtar masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama na hana jiragen daidaiku da ake bi bashin kudin fito aiki.

Sai dai jaridar Punch ta cikin gida ta ruwaito cewa mamallakan jiragen na neman kotu ta sake duba halaccin tursasa musu biyan kudin fiton, kamar yadda hukumar kwastam din ke ikirari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...