Da dumi-dumi: Kotun daukaka kara ta dawo da Binani a matsayin ‘yar takarar APC a Adamawa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Wata kotun daukaka kara ta mayar da Aishatu Binani a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Adamawa.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a watan Oktoba, wata babbar kotun tarayya da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa, ta soke zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da ya samar da Binani a matsayin dan takarar gwamnan jihar Adamawa.

Talla

Kotun ta Kuma bayyana cewar jam’iyyar APC a jihar bata da dan takarar gwamna a zaben 2023.

 

Kotun da mai shari’a Tanko Yusuf Hassan ya jagoranta ta yi watsi da hukuncin wata kotun tarayya da ya sauke takarar Aishatu Binani, da sanar da cewa APC ba ta da takara a zaɓen 2023.

 

A lokacin sanar da hukuncinsa, alkalin ya umarci a miƙa sunan Binani ga hukumar zaɓe mai zamanta wato INEC, a matsayin ‘yar takarar gwamnan APC a Adamawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...