Da dumi-dumi: Kotun daukaka kara ta dawo da Binani a matsayin ‘yar takarar APC a Adamawa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Wata kotun daukaka kara ta mayar da Aishatu Binani a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Adamawa.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a watan Oktoba, wata babbar kotun tarayya da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa, ta soke zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da ya samar da Binani a matsayin dan takarar gwamnan jihar Adamawa.

Talla

Kotun ta Kuma bayyana cewar jam’iyyar APC a jihar bata da dan takarar gwamna a zaben 2023.

 

Kotun da mai shari’a Tanko Yusuf Hassan ya jagoranta ta yi watsi da hukuncin wata kotun tarayya da ya sauke takarar Aishatu Binani, da sanar da cewa APC ba ta da takara a zaɓen 2023.

 

A lokacin sanar da hukuncinsa, alkalin ya umarci a miƙa sunan Binani ga hukumar zaɓe mai zamanta wato INEC, a matsayin ‘yar takarar gwamnan APC a Adamawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...