Kotu ta soke zaɓen fid da gwanin gwamna na APC a Taraba

Date:

Daga Ibrahim Ali Muhammad

 

 

Kotun tarayya da ke zamanta a Abuja babban birnin Najeriya ta soke zaɓen fitar da gwanin gwamna na jam’iyyar APC a jihar Taraba.

 

Alƙalin kotun mai shari’a Obiora Egwatu ya ce la’akari da hujjoji da shaidu da aka gabatar a gaban kotu, sun nuna cewa zaɓen fitar da gwanin da ka gudanar ranar 26 ga watan Mayun wannan shekara – wanda ya ayyana Sanata Emmanuel Bwacha a matsayin ɗan takarar – ba halastacce ba ne.

 

A watan da ya gabata ne dai wata kotun tarayya a birnin Jalingo ta soke zaɓen fitar da gwanin da jam’iyyar ta yi wa mista Bwacha, sakamakon ƙarar da ɗaya daga cikin ‘yan takarar ya shigar a gaban kotun yana ƙalubalantar sahihancin zaɓen.

Talla

 

Duka kotunan biyu a hukunce-hukuncen da suka yi sun bayar da umarnin ga uwar jam’iyyar da ta sake shirya wani sabon zaɓen fitarda gwani a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...