Kotu ta soke zaɓen fid da gwanin gwamna na APC a Taraba

Date:

Daga Ibrahim Ali Muhammad

 

 

Kotun tarayya da ke zamanta a Abuja babban birnin Najeriya ta soke zaɓen fitar da gwanin gwamna na jam’iyyar APC a jihar Taraba.

 

Alƙalin kotun mai shari’a Obiora Egwatu ya ce la’akari da hujjoji da shaidu da aka gabatar a gaban kotu, sun nuna cewa zaɓen fitar da gwanin da ka gudanar ranar 26 ga watan Mayun wannan shekara – wanda ya ayyana Sanata Emmanuel Bwacha a matsayin ɗan takarar – ba halastacce ba ne.

 

A watan da ya gabata ne dai wata kotun tarayya a birnin Jalingo ta soke zaɓen fitar da gwanin da jam’iyyar ta yi wa mista Bwacha, sakamakon ƙarar da ɗaya daga cikin ‘yan takarar ya shigar a gaban kotun yana ƙalubalantar sahihancin zaɓen.

Talla

 

Duka kotunan biyu a hukunce-hukuncen da suka yi sun bayar da umarnin ga uwar jam’iyyar da ta sake shirya wani sabon zaɓen fitarda gwani a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...