IPMAN tace tallafin man fetur ba mai ɗore wa ba ne a kasar nan

Date:

 

 

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta ƙasa (lPMAN), ta ce tallafin da ake biya a kan man fetur ba dawamamme ba ne.

 

Mike Osatuyi, Kwanturolan ayyuka na kasa na lPMAN, a wata hira da kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) a yau Litinin a Legas, ya yi Allah wadai da biyan tallafin man fetur.

 

Osatuyi ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karin farashin man fetur a gidajen mai a fadin kasar nan.

Talla

Ya ce gwamnatin tarayya ta kashe Naira tiriliyan 20.51 a kasafin kudin shekarar 2023 a kan kudaden shiga na Naira tiriliyan 9.7, inda ya bar gibin Naira tiriliyan 10.78.

 

Osatuyi ya ce gwamnati na fatan bayar da tallafin man fetur har zuwa watan Yunin 2023 kan kudi Naira tiriliyan 3.6, a kan N435 na farashin dala na babban bankin Najeriya (CBN).

 

“A halin yanzu, farashin a hukumance na CBN ya kai kusan N445 zuwa dala daya wanda ya haura N435 zuwa dala da aka ƙiyasta a kasafin kudin shekarar 2023,” inji shi.

Ranar ciwon Suga: Yara da yawa na kamuwa da cutar a Nigeria -Masana

Ya ce tsarin bayar da tallafin ya haifar da ƙaruwar giɓin kasafin kuɗi tare da haifar da koma baya ga rancen tattalin arziki.

 

Ya kuma ce tallafin ya sa fasa-kwaurin man fetur ya zama sana’a da a ke rububi saboda ribar da ake samu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...