Kar ku bari ‘yan Kwankwasiyya su yi amfani da karamin rikicin dake cikin mu – APC ta Kano ta gargadi ‘ya’yan ta

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Jam’iyyar APC a jihar Kano ta zargi ‘ya’yan jam’iyyar adawa ta NNPP Kwankwasiyya da yin amfani da wata ‘yar rashin jituwa a jam’iyyar APC mai mulki domin kara haifar da rashin jituwa.

 

Ya ce yayin da dattawan jam’iyyar suka sasanta rikicin cikin ruwan sanyi, ‘yan Kwankwasiyya da ke tsorata da karfin jam’iyyar APC a jihar suna ta yada farfaganda don zafafa lamarin.

 

Sanarwar gargadin ga ‘ya’yan jam’iyyar APC ta fito ne ta wata sanarwa da kwamishinan yada labarai kuma kakakin yakin neman zaben Gawuna/Garo Com. Muhd Garba a ranar Alhamis.

Talla

Ya ce akwai sahihan bayanai da ke nuna cewa kungiyar Kwankwasiyya har ta kai ga lalata fastocin yan APC , kuma ta yin hakan ne domin sake rura wutar rikicin da ake kokarin shawo kana ta.

 

Malam Garba ya yi nuni da cewa a ‘yan kwanakin da suka gabata ‘yan Kwankwasiyya sun yi ta watsa hotuna tare da ba su ma’ana mara kyau a kokarinsu na bata sunan jam’iyya mai mulki a jihar.

 

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, rashin jituwa ya zama ruwan dare a dukkan jam’iyyu, bai kamata a bar ‘yan adawa su yi amfani da su wajen kara haifar da fitina ga jam’iyyar ba.

 

Ya ce a daidai lokacin da al’ummar kasar nan ke tunkarar shekarar zabe, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da dan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, suna son ‘ya’yan jam’iyyar su tsaya tsayin daka tare da tabbatar da hadin kan ta don ci gaba da tafiya a kan turbar da ake ganin za ta samu nasara a dukkan matakai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...