Ku tabbatar da gwajin jini kafin ku daura Aure – Hakimin Ajingi ga limamai

Date:

Daga Zaharadeen Saleh

 

Hakimin Ajingi a masarautar Gaya dake nan jihar Kano Arewa maso yammacin Nigeria Alhaji Wada Muhammad Aliyu ya Umarci Limamai dake yankin karamar hukumar Gezawa da Minjibir da su daina daura Aure har sai sun tabbatar ma’auratan sunyi gwajin cutar amosani jini wato sikila.

 

Hakimin na Ajingi wanda kuma shine madakin Gaya ya bada wannan umarnin ne a wajen taron karawa juna sani daya shiryawa Dagatai da Limamai da masu unguwani na kananan hukumomin Gezawa da Minjibir.

 

Wada Muhammad Aliyu wanda Malam Abdulkadir Abdullahi Zanku ya wakilta, ya ce saboda mahimmacin da gwajin cutar amosanin jinin yasa hakimin Ajingi ya yi taro wayar dakai ga Dagatai da masu unguwanni harma da limamai.

Talla

Dakta Bello muhammad na babban asibitin garin Minjibir da Dakta Hamisu Musa Tahir sune suka gabatar da makala akan illar kin yin gwajin da kuma irin wahalar da iyaye zasu sha idan suka haifi yaro mai dauke da cutar Amosanin Jini.

 

Dakta Bello ya kara da cewa duk wanda yake da jini “AA” baya fuskantar barazar cutar ko kadan, yayin da wadda kuma yake da “As” to yana da Burbushinta wadda kuma yake “SS” yana da cutar don haka mai “As” da Mai “As” da Mai “SS” ba zasu iya yin aure ba.

 

Shima a nasa jawabin, hakimin minjibir Malam ismail Abdullahi A. Fulani ya sha alwashin wayar dakan alumma yakin karamar hukumar minjibir baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...