Da dumi-dumi: ASUU ta janye yajin aikin da ta yi watanni takwas tana yi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa wato ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi, makamar yadda jaridar The PUNCH ta rawaito.

Duk da cewa kungiyar ba ta fitar da sanarwar a hukumance ba, wakilin jaridar ya tattaro cewa an dauki matakin ne a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa ta kungiyar da aka gudanar a sakatariyar ASUU da ke Abuja.

Talla

Da yake zantawa da Majiyar Kadaura24, Wani da ya nemi a sakaye sunansa wanda kuma yana cikin taron, yace “Eh, an dakatar da yajin aikin”.

Talla

Da aka nemi karin bayani, majiyar ta ce, “Shugaban ASUU zai fitar da wata sanarwa a hukumance da safiyar nan”.

Talla

Kungiyar malaman ta fara yajin aikin ne a ranar Litinin, 14 ga Fabrairu, 2022.

 

Karin bayani na nan tafe…

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...