Daga Rukayya Abdullahi Maida
Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa wato ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi, makamar yadda jaridar The PUNCH ta rawaito.
Duk da cewa kungiyar ba ta fitar da sanarwar a hukumance ba, wakilin jaridar ya tattaro cewa an dauki matakin ne a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa ta kungiyar da aka gudanar a sakatariyar ASUU da ke Abuja.

Da yake zantawa da Majiyar Kadaura24, Wani da ya nemi a sakaye sunansa wanda kuma yana cikin taron, yace “Eh, an dakatar da yajin aikin”.

Da aka nemi karin bayani, majiyar ta ce, “Shugaban ASUU zai fitar da wata sanarwa a hukumance da safiyar nan”.

Kungiyar malaman ta fara yajin aikin ne a ranar Litinin, 14 ga Fabrairu, 2022.
Karin bayani na nan tafe…