Kwamishinan Noma na Kano ya yabawa Buhari saboda da Karrama A A Rano da lambar girmamawa ta OON

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kwamishinan harkokin noma na jihar kano Dr Yusuf Jibril Rurum J Y ya yabawa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari bisa yadda ya zabo Shugaban rukunin kamfanonin A A Rano Nigeria Limited Alhaji Auwalu Abdullahi Rano, Saboda karrama A A Rano da lambar girmamawa ta OON, sakamakon irin taimakon da yake yiwa al’umma Kasar nan baki daya.

 

Dr. Yusuf Jibril JY ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu Kuma aka aikowa kadaura24 a Kano.

 

“Babu shakka an yi amfani da chanchanta wajen zabo A A Rano domin bashi irin wannan lambar ta kasa wadda na yi Imani zata karawa Uban a wajena kwarin gwiwar cigaba da tallafawa rayuwar al’umma, domin shi ya yarda arzikin da Allah ya bashi, ya ba shi ne don ya tallafawa al’umma”. Inji kwamishinan Noma

Talla

 

Yace wannan karramawa da aka yiwa A A Rano ta tabbatar da cewa ba’a San rai ba wajen lalubo wadanda aka baiwa lambar girmamawar a wanann karon domin an baiwa dan kishin kasa mai jin tausayin mutane kuma wanda ya yarda a jingina da shi a tashi.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a ranar talatar da ta gabata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya mika lambar girmamawa ta OON ga Alhaji Auwalu Abdullahi Rano wanda hakan ce nuna cewa daga jiya talata dole ne a ƙarshen sunan A A Rano a Saka masa OON domin tabbatar da karramawar da shugaban kasa ya yi masa.

Talla

Kwamishinan harkokin noma na jihar kano Dr. Yusuf Jibril Rurum J Y yace a madadin sa da iyalansa da yan uwan da abokan arziki da al’ummar yankin kananan hukumomin Rano Kibiya da Bunkure yana taya Alhaji Auwalu Abdullahi Rano OON murnar samun Wannan karramawa da shugaban tarayyar Nigeria ya bashi.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta inganta walwala ma’aikatan dake kula da harkokin kudi – Babbar Akanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin jihar Kano ta ce za...

Fadar Shugaban Kasa ta magantu kan allunan tallan Tinubu da suka mamaye Abuja da Kano

Fadar shugaban Najeriya ta nesanta kanta daga wasu allunan...

Yansanda sun kama mafarauta huɗu ƴan asalin Jihar Kano a Edo

Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar Edo ta tabbatar...

Kotu a Amurka ta umurci FBI da hukumomin yaƙi da ƙwayoyi su saki bayanan bincike kan Tinubu

  Kotun Ƙoli ta Ƙasa ta Washington D.C. a Amurka...