Ganduje yace dole doka ta yi aiki akan dan Chinan da ya kashe Ummita

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Gwamnatin jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta ce za ta tabbatar da ganin shari’a ta yi aikinta a batun kashe Ummukhulthum Sani Buhari, matashiyar da ake zargin wani dan China da aikatawa.

Dr. Abdullahi Umar Ganduje yayin wani jawabi a fadar gwamnatin jihar ya ce “Zub da jini (ne, don haka) dole maganar shari’ah ta shigo” kuma sai doka ta yi aikinta.
Talla
Ya ce tuni suka sa aka kama mutumin da ake zargi Mista Geng Quanrong, bayan mutane sun damke shi a gidansu marigayiyar ranar Juma’a.
Bayanai sun ce lamarin ya faru ne ran Juma’a da dare, inda Geng Quanrong dan shekara 47 ya kutsa kai gidansu Ummita a unguwar Kabuga cikin karamar hukumar Gwale.
Talla
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce tana ci gaba da gudanar da bincike, inda ta mai da batun zuwa babban sashen binciken manyan laifuka bangaren kisan kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...