Inganta tsaro: Gwamnatin jihar Katsina ta horas da yan banga sama da dubu daya a jihar

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

An gudanar da bikin yaye ‘yan banga 600 da gwamnatin jihar Katsina ta dauki nauyin horaswa

Taron yaye yan bangar dai ya gudana ne a sansanin jami’an tsaro na NSCDC dake birnin Katsina inda daman nan ne aka ba su horon.

Da yake jawabi a wurin taron, Gwamnan jihar Katsina, Rt Hon Aminu Bello Masari wanda Sakataren Gwamnatin jihar ta Katsina, Alhaji Muntari Lawal ya wakilta ya yabawa mutanen da suka nuna sha’awar su ta shiga aikin bangar domin su taimakawa al’ummar su.

Haka zalika, Gwamnan ya kuma sha alwashin cigaba da mayar da hankali wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihar ta hanyar bayar da dukkan gudummuwa da goyon bayan da za’a bukata.

Talla

Gwamnan ya kara da cewa yanzu haka gwamnatin ta ware Naira biliyan 1 da miliyan 500 domin gudanar da ayyukan da suka shafi tsaron al’ummar jihar.

Tun da farko mai ba Gwamna shawara kan harkokin tsaro, Malam Ibrahim Katsina ya jinjinawa jami’an rundunar ta NSCDC bisa horon da suka ba yan bangar wanda yace zai taimaka sosai wajen shawo kan matsalar da ta addabi jihar Katsina.

Talla

Haka zalika Ibrahim Katsina ya bayyana cewa daga yanzu kam ba bu sauran sassauci daga gwamnati da al’ummar jihar Katsina ga yan bindiga tunda dai sun zabi yin fito-na-fito da su.

 

Mai ba Gwamna shawarar ya kuma bayyana cewa kawo yanzu gwamnatin ta horar da yan bangar 1,100 daga cikin mutane 3,000 da gwamnatin ta yi niyyar horarwa idan aka hada da wadannan 600 da aka yaye yau.

A jawaban su daban-daban, shugabannin hukumomin tsaron da suka magantu a yayin taron sun yaba da yadda shirin horaswar ya gudana cikin dan karamin lokaci kuma aka samu abunda ake so.

Abubuwan da suka gudana a wurin taron sun hada da atisaye da yan bangar suka gudanar wanda ya burge dukkan mahalarta taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...