Bayan amsa laifin sa, Yan Sanda sun fara bincike kan kisan da dan china ya yiwa wata budurwa a kano

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta tabbatar da mutuwar matashiyar nan mai suna Ummukulsum Sani Mai shekaru 22 mazauniyar Janbulo dake birnin Kano .

Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu Kuma aka rabawa manema labarai a ranar Asabar.
SP Abdullahi Kiyawa ya ce sun samu kiran gaggawa a ranar juma’a 16 ga watan Satumba 2022 , da misalin karfe 9:00pm na dare daga unguwar Janbulo , Inda aka fada musu cewa wani ɗan ƙasar Chana mai suna Geng Quanrong mai shekaru 47 mazaunin Nasarawa dake Kano yaje har gidan su matashiya ya hallakata, sakamakon rashin jituwa da ta shiga tsakanin su , Inda ya yi amfani da wuƙa yaji mata munanan raunuka ɗaya a wuyan ta sauran kuma a sassan jikinta.
Talla
” Bayan samun rahotanne Kwamishinan yan sandan jahar Kano CP Abubakar Lawan ya tura tawagar jami’an yan sanda ƙarƙashin jagorancin Baturan yan sanda na Ɗorayi Babba SP Ibrahim Hamma, inda suka garzaya da ita asibitin Murtala Muhammad Kano wanda likita ya tabbatar da mutuwar ta shi kuma wanda ake zargin an kama shi” . Inji SP Kiyawa
Talla
Kakakin Rundunar yan sandan yace tuni Kwamishinan yan sandan jahar Kano ya bada umarnin dawo da batun babban sashin gudanar da bincike na aikata manyan laifukan kisan kai dake Bomapai domin faɗaɗa bincike. Kuma yace tuni shi Wanda ake zargi ya fara yiwa jami’an su bayanin yadda lamarin ya faru,kuma ana cigaba da bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...