An kama wasu na lalata a tsakiyar tashar mota a Gusau dake Zamfara

Date:

Jami’an Hisbah a Jihar Zamfara sun kama wasu mutum biyu mace da namiji waɗanda ake zarginsu da lalata a tsakiyar wata tashar mota da ke birnin Gusau na Jihar Zamfara.

 

Kafar watsa labarai ta PRNigeria ta ruwaito cewa waɗanda ake zargin sun yi lalatar ne tsirara ba tare da la’akari da wani na kallonsu ba.

 

Sakamakon haka ne jama’ar da ke tashar motar suka yi sauri suka ankarar da jami’an Hisbah waɗanda a cikin gaggawa suka isa tashar suka yi awon gaba da su.

Talla

 

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce lamarin ya faru ne bayan namijin ya ƙalubalanci matar kan cewa ya fi ta rashin kunya, inda ita ma ta ƙalubalance shi, wanda daga nan suka soma wannan aika-aika.

 

Tuni dai aka gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban Kotun Shari’ar Musulunci ta Kankuri da ke garin Gusau.

 

A wani bidiyo da kadaura24 ta gani na hira da aka yi da waɗanda ake zargin, namijin da ake zargi ya ce bai san yadda aka yi hakan ta faru ba domin tun a farko ya je wurin wani biki ne inda daga nan ne yake kyautata zaton aka ba shi wani abu ya sha.

 

Talla

Ita kuwa macen cewa ta yi wannan abin ba halinta bane inda ta ce hasali ma sana’ar sayar da sanduna take yi.

 

Ta bayyana cewa idan ba ta samu cinikin sandunan bane take shiga wannan hali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...