Hukumar Hisbah a Kano ta kama mata da maza 23 a wasu wuraren masha’a dake Nasarawa G R A

Date:

Daga Aisha Abubakar Mai agogo
Dakarun hukumar Hisbah a jihar Kano masu hani ga munanan aiyukan, da kuma yin nuni ga kyawawa, a Daren jiya su ka kai sumame a gidajen 3 da ake zargi, samari da yan mata kan hadu su sha shisha da sauran kayan sa maye, daga bisani su aikata masha’a.
Tun da fari, Babban kwamandan hukumar Hisbah, Dr Harun Muhammad Sani Ibn sina yace makwabtan wadan nan gidaje da ake zargi sune suka kaiwa hukumar korafi, a lokuta daban-daban, tare da nuna takaicin yadda ake barin kananan yara shiga irin wancan gida.
A lokacin sumamen an sami nasarar cafke matasa 23 maza 4 sai yan mata 19 a lokacin da suke tsaka da busa tabar shisha, inda Dakarun Hisbah ba su yi wata-wata ba su ka damko su izuwa shalkwatan hukumar Hisbah.
Bincinken da Dakarun Hisbah na farin kaya su ka gabatar, ya tabbatar da cewa ana Shan shisha da sauran kayan sa maye, baya ga aikata badala a gidan.
Wuraren da aka damko matasan sun hadar da na titin Tukur road a unguwar nasarawa, da na titin sultan road, shi ma a unguwar nasarawa, da Kuma zuwa asibitin Nasarawa wato hospital road.
A cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran hukumar Lawan Ibrahim fagge ya aikowa kadaura24, yace Babban kwamandan hukumar Hisbah, Dr. Muhammad Sani Ibn Sina ya yi tsokaci, inda ya ba da tababbacin cigaba da kai sumame har ma da daukan matakan shari’a a kan irin wadan nan gidajen.
Sannan ya gargadi iyaye tare da Jan kunnen matasa da su guji jefa kan su cikin aiyukan masha’a domin samun shuwagabani na gari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...

Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Daga Sharifiya Abubakar   Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro...

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

  Yusuf Galambi dan majalisar wakilai ya sauya sheka daga...