Kungiyoyin kare hakkin dan Adam sun yi kira ga gwamnatin tarayya ta rushe kungiyar ASUU

Date:

Daga Abdulhamid Habib Isa Tukuntawa

 

Daraktan Gamayyar kungiyoyin kare hakki dan Adam na kasa Kuma Shugaban Global Community for human right Karibu Yahaya lawan kabara yace kamata ya yi gwamnatin tarayya ta rushe kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASSU.

 

Karibu yahaya kabara ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ya yi da wakilin Kadaura24 a Kano.

 

Yace yajin Aikin da kungiyar ke yi sanyawa matasa da yawa Cikin mawuyacin hali, wanda hakan ya Sanya matasan sun shiga hanyoyin da basu dace ba.

Talla

” Daga yanzu dole mu sauya akalar kiyaye-kirayen da muke, Kuma zamu matsa lambar akan dole gwamnati ta zama ko Malaman ASUU ko Kuma daliban kasar nan”. Inji Kabibu Yahaya

 

Yace kamata yayi gwamnatin tarayya ta ɗauki irin matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka na tilastawa malaman su koma aiki ko Kuma ta sallame su ta sake daukar wasu malaman.

 

Talla

” Idan gwamnatin ta ki daukar shawarar da muka bata, to su sani Matasa da yawa zasu lalace kuma kamar yadda wasu suka fara, Kuma lalacewar matasan barazana ce sosai ga Zaman Lafiyar kasar nan da ma cigabanta”. Inji Karibu Yahaya lawan

 

Karibullah kabara ya ce su dai Masu kare hakkin dan Adam basa goyon bayan gwamnatin tarayya ta ci gaba da lallashin Yan kungiyar ASUU ” kawai muna so a Kore su a kawo wasu ko kuma a a tilasta musu su koma bakin aiki”

 

Sannan yayi kira ga daliban da abun ya shafa dasu kara hakuri da halin da suka tsinci kansu a ciki ind yace komai yayi farko zaiyi karshe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan zaben kananan hukumomin Kano

Kotun ɗaukaka kara dake Abuja, ta rushe hukuncin babbar...

Dole ne yan Nigeria su dage da yawaita addu’o’i a kwanaki 10 Zulhijja – Sheikh Muhd Nasir

Daga Usman Hamza Shugaban majalisar limaman masallatan juma'a na Nigeria...

Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...