GEP ta yabawa gwamnatin Kano bisa amincewa da daukar malamai mata 195

Date:

Daga Aliyu Abdullah Fagge

 

Wata Kungiya dake tallafawa Ilimin ‘ya’ya Mata ta yabawa gwamnatin jihar Kano bisa amincewa da daukar malamai mata 195 aiki karkashin ma’aikatar kananan hukumomi.

 

A cikin wata sanarwa da Shugabar shirin Hajiya Mairo Bello ta Sanyawa hannu Kuma aka aikowa kadaura24, Kungiyar ta kuma nuna matukar godiya ga uwargidan gwamnan jihar Kano Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje bisa kishin da take da shi na ilimin ‘ya’ya mata a jihar.

 

GEP ta yaba da yadda aka ware naira miliyan dari a cikin kasafin kudin shekarar 2022 domin daukar malamai mata dubu daya aiki.

 

Yanzu-Yanzu:Bayan Rantsar da sabbin kwamishinoni, Ganduje ya bayyana ma’aikatun su

Idan za a iya tunawa, ma’aikatar Ilimi da ta kasafi da tsare-tsare tare da hadin gwiwar ofishin PERL da ke Kano, a karkashin kulawar ofishin ci gaban kasashen waje da na Commonwealth (FCDO) tare da sauran manyan ma’aikatu da Hukumomin gwamnati sun aiwatar da tsare ba da ilimi ga kowa a shekarar 2021, Inda suka samar da wani cikakken tsarin gudanar da ayyukan shekara-shekara karkashin kulawar gamayyar Masu tallafawa Ilimin ‘ya’ya Mata (GEP) .

 

Masu tallafawar da haɗin gwiwar ma’aikatar kasafi da tsare-tsare da ta jihar sun ƙirƙiri wani kundin kasafin kuɗin ilimin ‘ya’ya mata tare da shigar da shi cikin kasafin kuɗi na 2022 a tsakanin Ma’aikatu da hukumomin gwamnati na jihar. An yi hakan ne domin a tabbatar da tsarin ilimin ‘yan mata a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

 

Talla

A tsarin da aka tsara, gwamnatin jihar ta ware naira miliyan 100,000.00 domin daukar ma’aikatan Masu NCE 105 da wadanda suka kammala karatun digiri 90.

 

GEP tace ta gamsu da tsarin da tuna da gwamnatin jihar Kano ta yi amfani da shi a shekarar 2018 Inda ta dauki malamai mata 1,196 wadanda su ke da shedar karatu ta NCE a fadin jihar.

 

Kazalika kungiyar ta nuna gamsuwarta da yadda gwamnati ta raba katon 500 na litattafai da kayan kula da mata da tsafta ga makarantun sakandaren mata 15 da ke fadin shiyyoyi guda 3 da ake da su a Kano.

 

Talla

Haɗin gwiwar ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa gyara 14 daga cikin motocin bas ɗin da suka lalace domin daukar ‘ya’ya mata zuwa makaranta.

 

Wannan ci gaban ya samo asali ne sakamakon ci gaba da bayar da shawarwari ga hukumomin gwamnati da kungiyoyin ‘yan kasa suka yi don kara kaimi ga kara saka hannun jari kan ilimin ‘ya’ya mata.

 

Kungiyar ta kuma taya sabon kwamishinan ilimi murna

 

GEP ta aike da sakon taya murna ga sabon kwamishinan ilimi Alhaji Ya’u ‘Yanshana tare da fatan zai kara inganta Ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jagorancin da zai yi wa ma’aikatar.

 

Don haka ta yi kira ga sabon kwamishinan da ya yi amfani da kwarewarsa wajen ganin an dauki malamai mata 195 aiki kamar yadda aka yi alkawari a shekarar 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...