Bayan fitar Shekarau daga NNPP, wa zai yiwa Jam’iyyar takarar Sanatan Kano ta tsakiya ?

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A ƙarshe makon jiya ne farkon  Sanatan kano ta tsakiya Malam Ibrahim Shekarau ya aikewa da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC takardar ajiye takarar Sanatan Kano ta tsakiya da yake a jam’iyyar NNPP, gabanin ya bar jam’iyyar bisa zargin rashin adalci da yake ga jagoran jam’iyyar na ƙasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

 

Tun bayan faruwar lamarin, al’umma ke tofa albarkacin bakinsu akan wanda ya kamata ya gaji wannan takara, musamman tsohon dan takara, Aliyu Sani Madaki, wanda kwankwasiyya ta tsayar a kakar zaben shekarar 2019 da ya gabata.

 

Hal ila yau, akwai masu fatan Sanata Rufai Sani Hanga ya samu wannan tikiti, akwai masu ganin Sha’aban Ibrahim Sharada ya ajiye takararsa ta gwamna a ADP domin yazo NNPP a bashi wannan tikiti, da sauran mutane da masoya ke musu fatan alheri.

 

Bisa doka, jam’iyya na da kwanaki 14 ne daga ranar da dan takara ya tura takardar ajiye takara ga INEC, daga nan kuma sai a shirye sabon zaɓen fidda gwani, duk cikin kwanaki 14.

 

Nasara Radio ta rawaito a yanzu dai abin jira a gani, shi ne lokaci, domin bayyana wanda zai samu wannan tikiti cikin mutanen da ake yiwa zawarci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...