Wasu Magoya bayan Shekarau da suka shiga NNPP tare sun jaddada goyon bayan su ga Kwankwaso

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Kimanin mabiya 45 ne da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar NNPP tare da Sanata Ibrahim Shekarau su ka yanke shawarar ci gaba da zama a jam’iyyar da nufin mara mata baya domin samun nasara a zaɓukan da ke tafe.

 

Da ya ke karanta sanarwar bayan taro a madadin ƴan siyasa 45 jim kadan bayan kammala taro, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Karaye/Rogo ta tarayya, Haruna Dederi, ya ce mambobi 45 da suka rattaba hannu kan takardar, sun yanke shawarar ci gaba da zama a jam’iyyar NNPP domin nuna ƴancinsu na ƴan ƙasa, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, ya jajanta wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa

 

Dederi, wanda lauya ne, ya bayyana cewa, “Mun haɗa kai domin yanke shawarar ci gaba da zama a jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano tare da jajircewarmu wajen ganin jam’iyyar ta kai ga nasara a babban zabe mai zuwa. Za mu ci gaba da sadaukarwa ga babbar jam’iyyarmu don kara karfafa tushen goyon bayan ta.

Yanzu-Yanzu : Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon ruftowar wani gini a kasuwar Beruet dake kano

 

“Jam’iyyar NNPP ba ta da kishiya ga duk wani mabiyin jam’iyya da jagoranci mai da ya san me ya ke yi. Wannan gaskiya ce da aka sani a ciki da wajen ƙasa . Muna kira ga daukacin al’ummarmu da su ci gaba da ba mu hadin kai domin mu karkata ga al’amuran jiharmu domin ci gaban al’ummarta tare da ceto al’ummar kasar daga halin da ake ciki na rugujewa.

“Mun amince da haƙƙin ɗan ƙasa na yin zaɓar ra’ayin sa na yin amfani da ‘yancinsa na tarayya kamar yadda kundin tsarin mulkinmu ya tanada.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...