Wani direban adaidaita sahu ya rasa ransa, bayan ya fada wani kogi a kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

 

Wani matashi dan shekara 25 mai suna Ammar Ibrahim ya nutse a wani kogi a kauyen Tattarawa da ke Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Saminu Abdullahi ya fitar a yau Laraba a Kano.

 

Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne a jiya Talata .

 

“Mun samu kiran gaggawa da misalin karfe 11:34 na safe daga wani Muhammad Sani kuma mun aika da tawagar mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 11:55 na safe.

 

“Direban adaidaitasahu din da ke kan hanyarsa ta komawa Kano, ya yi fakin a gefen titi kusa da wani kogi da nufin wanke babur din, amma sai tsautsayi ya ja shi cikin kogin.

 

“Ya yi ƙoƙari da yawa don ya tsere amma hakan bai yiwu ba,” in ji Abdullahi.

 

Ya ce an fito da marigayi Ibrahim daga cikin ruwan a sume kuma daga baya aka tabbatar da rasuwarsa.

 

Abdullahi ya ce an mika gawar ga Sifeto Jerry Mathew na ofishin ‘yan sanda na Dawakin Tofa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...