Yanzu-Yanzu : Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon ruftowar wani gini a kasuwar Beruet dake kano

Date:

Daga Jafar Adam Jikamshi

 

Wani gini ya rufta kan mutane ana tsaka da kasuwanci a kasuwar wayar hannu ta Beruet dake birnin Kano.

 

Kadaura24 ta rawaito Wani shaidan gani da Ido Mai suna Nura Mai Mai ya shaidawa wakilmu cewa lamarin ya faru ne da misali karfe 4 saura da dai lokacin da mutane suka ta harkokinsu a kasuwar.

Wallahi Muna zaune kawai sai muka ji rugugu ashe ginin da yake kusa da masallacin yan izala  na kasuwar, Kuma akwai mutane da yawa da Ginin ya fada kansu” inji Muhd Nura Mai Mai

 

Muhammad Nura ya ce shi ma Allah ne ya kiyaye shi domin bai dade da barin wajen da lamarin ya faru ba, Kuma Gini ne da ba’a dade da kammala shi ba Kuma benene Mai hawa 2.

 

Yanzu haka dai jami’an hukumar kashe gobara ta jihar kano ta Isa wajen domin ceto wadanda ginin a afka musu .

 

Duk kokarin da mukai na jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar kano ya ci tura, domin mun kirawo shi Amma wayarsa bata shiga .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...