Sojoji Sun Tarwatsa Yan Bindinga a Kaduna

Date:

Wata tawagar rundunar sojin Najeriya ƙarƙashin Manjo Janar Taoreed Lagbaja hadin gwiwa da wasu jami’an tsaro sun fatattaki ƴan bindiga a wasu yankunan jihar Kaduna, mai fama da ƙaruwar hare-haren ƴan bindiga.

 

Rundunar ta kai samame kan yankunan Buruku da Udawa da Manini da Birnin Gwari da Doka da Maganda da Kuyello da Dogon Dawa jiya Litinin.

Akwai yiwuwar gwamnatin tarayya zata ciyo bashin Naira Tiriliyan 11a shekara ta 2023 – Ministar Kudi

 

Yayin ɓata-kashin, sojojin sun ci ƙarfin ƴan bindigar ta hanyar amfani da manyan makamai wajen halaka ɗaya daga cikinsu, wasu uku kuma aka cafke su da ransu sai kuma wasunsu da suka tsere da raunuka.

 

Sanarwar da kakakin rundunar Kanar Onyema Nwachukwu ya fitar ta ce sojojin sun kuma gano bindiga ƙirar AK47 da alburusai da baburan hawa 18.

Ambaliyar ruwa: Gwamnatin Kano za ta rushe gine-gine da a ka yi kan hanyoyin ruwa

Rundunar sojin ta kuma nemi hadin kan al’umma wajen bankado mutanen da aka gansu da harbin bindiga tare da kjai rahoto ga hukumomin tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...