Sarkin Kano ya Jinjinawa Masu Gina Asibitoci Masu Zaman Kansu a Kano

Date:

Daga Maryam adamu Mustapha

 

Sarkin Kano, ya jinjinawa masu hannu da shuni da suke gina asibitoci domin tallafa wa talakawa a cikin al’umma.

 

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukaci masu hannu da shuni a cikin al’umma da su hada karfi da karfe a fannin lafiya don inganta lafiyar al’ummar jihar kano da kasa baki daya.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, yace  Aminu Ado Bayero  ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake duba sabon Asibiti mai zaman kansa da wani Dan kishin kano ya gina a birnin Kano.

 

2023: Bayan ficewa daga NNPP, Shekarau ya bayyana matsayin takarar sa ta Sanata

 

Yace ya yaba da kokarin wanda ya kirkiro asibitin na taimakawa al’ummar jihar Kano da ma kasa baki daya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa bangaren kiwon lafiya zai bada gudunmuwa domin taimakawa al’umma.

Ambaliyar ruwa: Atiku ya bada tallafin Naira Miliyan 50 ga yan kasuwar K/ Kwari

 

A nasa jawabin, shugaban asibitin, Dakta Muhammad Garba, ya ce ya kafa asibitin ne domin saukaka wa al’umma musamman marasa galihu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...