Sarkin Kano ya mika ta’aziyyar rasuwar Sarkin Funakaye Alh. Muazu Muhd Kwairanga

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi.

 

 

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai, Yan uwa, al’ummar Masarautar Funakai da na jihar Gombe gaba daya bisa rasuwar Sarkin Funakaye Alhaji Muazu Muhammed Kwairanga, wanda ya rasu a yau Lahadi 28 ga watan Agusta, 2022.

 

Sanarwar mai dauke da sa hannun Babban Sakataren Yada Labarai na Masarautar Kano Abubakar Balarabe Kofar Naisa ta ce Majalisar Masarautar Kano da na Jihar Kano sun kadu Sosai da samu labarin rasuwar Mai Martaba Sarkin Funakaye Alhaji Mu’azu Muhammed Kwairanga a safiyar lahadi.

 

Rasuwa, a cewar Sarkin Kano, ta dauke shi a lokacin da kasar nan ta fi bukatar sa, inda ya jaddada cewa, “Wannan babban rashi ne ga al’umma a fadin kasar nan da ma sauran sassan Afrika baki daya”.

2023: NNPP Zata kwace Mulki Borno daga Hannun Gwamna Zulum – Kwankwaso

 

Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa marigayi Alhaji Mu’azu Kwairanga na jihar Gombe, yasa kyakyawan aikin sa ya bishi ya kuma baiw al’ummar Masarautar Funakai juriyar Wannan babban rashi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...