Sarkin Kano ya mika ta’aziyyar rasuwar Sarkin Funakaye Alh. Muazu Muhd Kwairanga

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi.

 

 

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai, Yan uwa, al’ummar Masarautar Funakai da na jihar Gombe gaba daya bisa rasuwar Sarkin Funakaye Alhaji Muazu Muhammed Kwairanga, wanda ya rasu a yau Lahadi 28 ga watan Agusta, 2022.

 

Sanarwar mai dauke da sa hannun Babban Sakataren Yada Labarai na Masarautar Kano Abubakar Balarabe Kofar Naisa ta ce Majalisar Masarautar Kano da na Jihar Kano sun kadu Sosai da samu labarin rasuwar Mai Martaba Sarkin Funakaye Alhaji Mu’azu Muhammed Kwairanga a safiyar lahadi.

 

Rasuwa, a cewar Sarkin Kano, ta dauke shi a lokacin da kasar nan ta fi bukatar sa, inda ya jaddada cewa, “Wannan babban rashi ne ga al’umma a fadin kasar nan da ma sauran sassan Afrika baki daya”.

2023: NNPP Zata kwace Mulki Borno daga Hannun Gwamna Zulum – Kwankwaso

 

Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa marigayi Alhaji Mu’azu Kwairanga na jihar Gombe, yasa kyakyawan aikin sa ya bishi ya kuma baiw al’ummar Masarautar Funakai juriyar Wannan babban rashi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...