Rundunar Sojin Nigeria ta Kori Sojojin da ake Zargi da Kisan Wani Malami a Yobe

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Rundunar sojin Najeriya ta kori wasu sojoji biyu bisa kisan wani malamin addinin musulunci, mai suna Sheikh Goni Aisami Gashua, a jihar Yobe.

 

Sojojin da aka kora sun hada da Lance Kofur John Gabriel da Lance Kofur Adamu Gideon.

Talla
Talla

Mukaddashin kwamandan da ke kula da bataliya ta 241 Reece dake Nguru a jihar Yobe, Laftanar Kanar Ibrahim Osabo, ya shaida wa manema labarai cewa kwamitin binciken hadin gwiwa da aka kafa tare da hadin gwiwar ‘yan sanda ne ya same su da laifin kisan malamin.

 

Kishi: Wata Mata ta Kashe Tsohon Mijinta a Jihar Kebbi

Ya ce an sallami sojojin biyu ne bisa tuhume-tuhume biyu na rashin yin ayyuka da kuma nuna kyama ga horon aikin.

Dole dan Kwangilar da ya Gina Gadar Lado ya Dawo ya gyara ta -Ministan aiyuka

Laftanar Kanar Osabo ya kara da cewa za a mika sojojin da aka kora a hannun ‘yan sanda a Damaturu domin gurfanar da su a gaban kotu.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Dungus Abdulkarim, a wata zantawa da manema labarai, yace an kama wadanda ake zargin dauke da bindigogi kirar AK-47 kuma suna hannun ‘yan sanda.

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da kisan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...