Ana Neman Hana mu Damar da Kundin Tsarin Mulkin Kasa ya Bamu a Dorayi Babba dake kano – Inji Yan Shi’a

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Wasu mabiya Shi’a a jihar kano sun roki gwamnati da jami’an tsaro a jihar kano da su Basu kariya don su gudanar da harkokin addininsu kamar yadda dokar kasa ta baiwa kowanne dan Nigeria.

 

Kadaura24 ta rawaito Sulaiman Gambo shi ne ya bayyana hakan lokacin taron manema labarai da suka gudanar a nan Kano a ranar Asabar.

 

Sulaiman Gambo yace a jiya juma’a wasu batagari sun je Inda suka gudanar da karatuttukansu da addu’o’i suka bankawa makarantar wuta ba tare da sun bar ko tsinke ba a cikin makarantar.

 

 

” Wasu da muke Zargin tunzura su akai sun zo sun gone mana kayiyaki Masu tarin yawa, wadanda suka hadar da janareto da litattafai da sauran kayan koyo da koyarwa da ma Sauran kayan amfani na yau da kullum suka Tara su wuri guda suka sa taya sannan suka gone su kurmu”. Gambo

 

Yace lamarin dai ya faru ne a wata makarantarsu dake unguwar Dorayi babba, Inda ya ce Wannan ba shi ne karon farko ba da aka yi musu irin wannan mummunan aikin wanda yace ba addinin musulunci ne ya koyar da su ba .

Kishi: Wata Mata ta Kashe Tsohon Mijinta a Jihar Kebbi

 

“Akwai wasu limaman masallatan juma’a da muke Zargin sune suka tunzura wadanda suka yi mana waccan ta’adi wanda yasa mukai asarar kimanin Naira Miliyan 3 da wani Abu” inji Sulaiman Gambo

 

Rundunar Sojin Nigeria ta Kori Sojojin da ake Zargi da Kisan Wani Malami a Yobe

Yace daman a bayan sun kai Kara wajen jami’an tsaro har ma tsohon kwamishinan yan sanda wanda ya ajiye aiki ya bada umarni ga DPO na Chaji ofis din Yan sanda na Dorayi babban da ya gudanar da bincike kan abubuwan da ake yi mana.

 

” Mu fa bama son tashin hankali saboda mu Musulmi Kuma musulunci ya hana tashin hankali, Amma ana so a hana mu damar da kundin tsarin mulkin kasar nan ya bamu na kowa yayi addinin da yake so cikin yan me yasa mu za’a rika yi mana haka?”.

 

Sulaiman Gambo ya suna kira da duk Masu fada a ji a yankin unguwar Dorayi babban da sauran masu ruwa da tsari da dauki matakan hana afkuwar hakan a nan gaba domin yin hakan shi ne zai tabbatar da dorewar Zaman lafiyan da ake da shi a jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...