2023: Takarar Sha’aban Sharada nake goyon baya a ADP Kuma zan bashi gudunmawa har ya ci zabe – Rarara

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Shahararren mawakin Siyasar nan Alhaji Dauda Kahutu Rarara yace ya dauki Sha’aban Ibrahim Sharada a matsayin Dan takarar sa na gwamna a  zaben shekara ta 2023 .

 

Kadaura24 ta rawaito Rarara yace yana da dalilai Masu yawa da suka sa zai goyi bayan takarar gwamnan kano ta Sha’aban Ibrahim Sharada.

 

Dauda Kahutu Rarara ya bayyana hakan ne yayin Wani taro da Sha’aban Sharada ya shirya a Kano .

Ganduje zai nada matashi mai shekaru 33 kwamishina a kano, waye shi ?

” A cikin dalilai na ko da daya na dauka ya isheni hujjar goyon bayan takarar Sha’aban Sharada, Amma yanzu lokaci bai yi ba da zan bayyana ba, nan gaba kadan zan fada kowa ya ki”. Inji Rarara

“Ina Wannan tafi Kuma da ni za’a yi ta har lokacin da Zamu je a rantsar da Sha’aban, zan Kuma bada gudanarwar wakoki kamar su “Malam Sha’aban” da Kuma Dan Karamin sauro”. Inji Rarara

 

Shura ta baiwa Shekarau sharudda 5 na sauya sheka zuwa PDP

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Sha’aban Sharada ya fice daga jam’iyyar APC Inda ya koma jam’iyyar ADP Kuma har ya sami takarar gwamnan Kano a jam’iyyar.

 

Abun mamakin dai shi ne yadda Rarara ya yi Shura wajen yiwa jam’iyyar APC wakoki da Kuma goyon bayan takarar Bola Tinubu a matsayin dan takararsa na shugaban kasa wanda kuma dan jam’iyyar APC ne, kwatsam sai ga shi ya bayyana goyon bayan takarar sa a jam’iyyar ADP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...