Guguwa: Gidaje da gine-gine 1,300 sun lalace a Jigawa

Date:

Daga Zainab Muhammad Darmanawa

 

Gwamnatin Jigawa ta ce gidaje 1,300 ne guguwar ta lalata a Ƙaramar Hukumar Kafin Hausa.

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya bayar da rahoton cewa, lamarin da ya faru a ranar Talata da daddare, ya yi ɓarna sosai.

 

Mataimaki na musamman ga Gwamna Muhammad Badaru kan ci gaban al’umma da taimakon jama’a, Hamza Muhammad, ya shaida wa NAN a yau Asabar cewa, sama da gidaje 1,300 ne ibtila’in guguwar ya afkawa, inda wasu su ka rushe gaba ɗaya, wasu kuma su ka lalace.

 

Da gaske ne Dan Kannywood Ali Artwork Madagwal ya Mutu ?

Muhammad ya ce guguwar ta kuma lalata wasu sassan babban asibitin yankin da matatar ruwa da kuma makarantu.

 

“Daga rahoton tantancewar da na samu jiya, baya ga wadannan, guguwar ta kuma lalata rufin babban asibitin Kafin Hausa na dakunan haihuwa da na gaggawa da na wasu makarantun yankin.

Shin Kun San Matashiyar da ke bayar da hayar kayan biki a Kano

“Haka kuma ya sauke wasu tankunan ruwa na sama, da kuma ɗaya daga cikin antenar sadarwa a yankin,” in ji Muhammad.

 

Sai dai ya ƙara da cewa an kai marasa lafiya a ɗakin haihuwar lafiya zuwa wasu wuraren kiwon lafiya.

 

Mataimakin ya kuma bayyana cewa, gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, SEMA da kuma hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa NEMA, sun kasance a yankin tun a ranar Laraba, inda suka tantance irin barnar da bala’in ya yi.

 

Wannan a cewarsa, domin baiwa gwamnati da hukumomi damar sanin irin barnar da guguwar ta haddasa, da nufin shiga tsakani da kuma bayar da tallafi ga wadanda abin ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...