Rashin tsaro: Masarautar Katsina ta Dakatar da Hawan Babbar Sallah

Date:

Daga Abubakar Dayyabu Safana

 

Majalisar Masarautar Katsina ta sanar da dakatar da Hauwan bukukuwan Sallah Babba a ranar Asabar.

 

Sanarwar dakatarwar ta fito ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Talata a Katsina, Mai dauke da sa hannun mataimakin sakataren majalisar, Sule Mamman-Dee.

 

Ya ce an dakatar da hawan ne saboda yanayin tsaro da ake fama da shi a jihar.

 

A cewar Mamman-Dee, Sarkin Katsina, Abdulmumini Kabir-Usman, ya nuna matukar damuwarsa kan matsalar tsaro a sassan masarautar inda ya ce zai halarci Sallar Idi ne kawai a ranar Asabar ba tare da hawan sallah ba.

 

Ya bayyana cewa Sarkin ya shawarci al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’o’in samun zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

 

Bikin Durbar dai ya samo asali ne tun shekaru aru aru da suka gabata, Shekaru kusan biyu kenan ba’a gudanar da hawan ba, saboda matsala ta tsaro data addabi al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...