Daga Zara Jamil Isa
Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta jaddada cewa tana da ƙwarin gwiwar kwashe dukkan maniyyatan da suka rage a ƙasa yayin da ake shirin rufe jigilar mahajjata zuwa Saudiyya a daren yau Lahadi.
Zuwa yanzu maniyyata fiye da 18,000 ne suke jiran a kai su Saudiyyar, yayin da hukumar ta NAHCON ta kwashe 25,361 kawai daga cikin fiye da 43,000 na alhazan Najeriya.
BBC Hausa ta rawaito cewa Daga ƙarfe 12:00 na daren yau Lahadi wa’adin rufe jigilar maniyyata zai cika, kodayake wasu kamfanonin sufurin jirage sun samu ƙarin awanni na ci gaba da aikin.
Yayin wani taron manema labarai a Abuja a yau Lahadi, NAHCON ta ce tana da ƙwarin gwiwar kwashe maniyyatan da suka rage zuwa ƙasa mai tsarki don gudanar da aikin Hajjin bana.