Daga Zara Jamil Isa
Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta bayyana cewa duk da kokarin da Najeriya ta yi, don samin karin kujerun aikin Hajjin bana abun ya ci tura.
Har ila yau, NAHCON ta ce kokarin diflomasiyya da tayi don a bar jami’an da suka haura shekaru 65 su je Saudiyya don taimakawa alhazai a yayin aikin Hajjin bana.
Kakakin Hukumar NAHCON, Fatima Sanda Usara ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa data sanyawa hannu a ranar Talata, inda ta ce Saudiyya ta ki amincewa da bukatar.
Hukumomin Saudiyya sun ware sama da kujeru 43,000 ga maniyatan Najeriya a bana, tun bayan shafe shekaru biyu ba tare da an baiwa kasashe izini ba shiga kasar ba.
NAHCON ta raba kason da aka bata ga daukacin jihohin kasar nan 36 da babban birnin tarayya Abuja da dakarun soji da kuma yan jirgin yawo, lamarin da ya haifar da rikici a tsakanin kungiyoyin da NAHCON. hukumar ta bukaci karin kujeru 5000 daga ma’aikatar Hajji da Umrah domin magance matsalar.