Hajjin bana: Mun Amincewa Jirgin Max Air ya yi jigilar maniyatan Kano – Muhd Abba Danbatta

Date:

Daga Zara Jamil Isa

 

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta bada tabbacin cewa kamfanin jirgin sama na Max air ne zai yi jigilar maniyatan jihar nan zuwa kasa mai tsarki.

Kadaura24 ta rawaito Sakataren zartarwa na hukumar Alhaji Muhd Abba Danbatta ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a Kano.
Alhaji Muhd Abba Danbatta yace sun kammala tattauanawa da hukumar kula da aikin Hajji ta kasa Nahcon inda suka tsayar da matsayar kamfanin jirgin sama na Max air shi ne zai yi jigilar maniyatan jihar Kano zuwa kasa mai tsarki.
Talla
Yace dama rashin kammala tattauanawa da hukumar Nahcon ne ya hana hukumar jin dadin alhazai ta Kano ta sanar da kamfanin da zai yi jigilar maniyatan jihar.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa hukumar jin dadin alhazai ta kano taki amincewa da kamfanin jirgin na Azman saboda da wasu dalilai.
Babban sakataren ya kuma ce zasu fara tantance lafiya maniyatan su a gobe litinin domin tabbatar da cewa ba’a sami alhazai masu dauke da cutar murar burrai da cutar corona ba.
Ya bada tabbacin kowanne lokaci daga yanzu za’a fara jigilar maniyatan jihar Kano zuwa kasa mai tsarki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kansila a K/H Garum Mallam ya rabawa marayu 300 kayan Sallah

Daga Safiyanu Dantala Jobawa   Sama da yara mayaru 300 ne...

Sallah: Baffa Babba ya raba buhu 2,000 na Shinkafa ga Kungiyoyin Tinubu a Kano

Babban daraktan cibiyar kula da ingantuwar aiyuka ta kasa...

Babbar Sallah : Kansilan Lajawa ya raba Naira dubu 500 ga al’ummar mazabarsa

Daga Nura Adam   Kansilan mazabar Lajawa a karamar hukumar Wudil...