Mallakar katin zabe wajibi ne ga dan kasa na gari – Isa Zaura

Date:

Daga Shehu Sulaiman Sharfadi

 

Wani Dan rajin cigaban matasa Isa Umar ya yi kira ga daukacin matasan  jihar kano da su yi kokari su mallaki katin zabe  duba  da cewar shi ne kadai abin da dan kasa zai kare yancinsa wajen zabar shugabanin  nagari a zaben shekara  ta 2023.

 Isa Umar Zaura wanda guda ne cikin jagororin tafiyar siyasar gidan A.A Zauna ya bayyana hakan ne a zantawarsa da wakilin Kadaura24 a Kano.

Jagoran ya bayyana  cewar shekaru 22 bayan dawowa mulkin demokaradiyya mafi akasarin matasan wasunsu suna da shekaru goma sha shida zuwa sha bakwai don haka ya zama wajibi agaresu su mallaki Katin zabe don zabar  shugabanni nagari a zaben  shekara  ta 2023.
Alhaji Isa ya kuma bukaci matasan su rungumi  sana’o’i komai  kankantarsu don kare mutuncinsu  da kuma kaucewa fadawa hannun batagari wadandaKeyin amfani  dasu don biyan bukatun kansu musamman ma duba da  karatowar zaben shekarar 2023.

 Daga karshe yayi kira ga al’ummar  kasar nan da su tabbata da cewa sun duba cancanta yayin zaben  shugabanni da kuma yin addu’ar Allah ya zabawa jihar Kano dama kasa baki daya shugabanni nagari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...