Kwankwaso ya Musanta zargin karbar kudin Delegate PDP a hannu Wike

Date:

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP, Rabiu Kwankwaso, ya musanta sayar da wakilan zaɓe na Kano ga ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Nyesom Wike.

Duk da cewa a na zargin shugabancin PDP, ƙarƙashin jagorancin Shehu Sagagi a jihar Kano na biyayya ga Kwankwaso, amma Kadaura24 ta tattaro bayanai cewa ba a baiwa Kwankwaso kuɗin da a ke raɗe-raɗin an bashi ba, wakilan a ka baiwa.

Wata kafar yaɗa labarai ce ta yi zargin cewa Wike ya sayi wakilan Kano 45 da za su halarci babban taron zaɓen ɗan takarar shugaban kasa na PDP kan dala 15,000 kowanne.

Sai dai kuma Kwankwaso, a wata sanarwar da hadiminsa, Ibrahim Adamu ya fitar a jiya Asabar domin mayar da martani a kan rahoton, ya suffanta rahoton a matsayin ƙarya da kuma yarfe.

Ya ce ” Abu ne sananne cewa, a ranar 29 ga Maris, 2022, Mai Girma Sanata Mohammed Rabiu Musa Kwankwaso ya yi murabus daga jam’iyyar PDP tare da yin jawabi ga taron manema labarai na kasa kan hakan. Don haka shirme ne ma a ce dan takarar shugaban kasa zai zai bauwa shugaban jam’iyyar adawa da kudi domin ya sayi wakilan jam’iyyarsa.

“Muna ma su musun ta wannan zarge-zargen gaba dayansa kuma muna kira ga jama’a da su yi watsi da shi a matsayin wani launi na tunani na wata jaridar yanar gizo. Don haka muna ba wa jaridar nan sa’o’i 48 da ta cire labarin na na karya tare da bayar da hakuri a cikin jaridu uku na kasa.

“A kan wannan batu na sama, muna kira ga jama’a da su yi watsi da bayanan karya domin kwata-kwata karya ce kuma an yi ne domin rikitar da al’umma,” in ji sanarwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...