Bayan tafiya Umarah Ganduje ya sake Mika mulkin Kano ga Mataimakinsa Gawuna

Date:

Daga Mubaraka Aliyu Ibrahim
 Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya tafi kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umarah a saboda haka ne ya mika ragamar Mulkin Kano ga Mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna.
Hakan na kunshe ne cikin wata Sanarwa da Babban sakataren yada labaran Gwamna Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24.
Sanarwar tace Yayin da Gwamna Ganduje yake kasar Saudiyya mataimakinsa Nasiru Yusuf Gawuna zai kasance a matsayin mukaddashin Gwamnan kano.
 An umurci dukkan Ma’aikatu, Ma’aikatu da Hukumomi Gwamnatin kano da su yi biyayya da Mukaddashin Gwamna domin tafiyar da jihar yadda ya dace m.
 Don haka Gwamna Ganduje ya bukaci kowa da kowa ya yi amfani da kwanaki Goma na karshe na watan Ramalana, domin neman gafarar Allah, da addu’ar samun zaman lafiya ga jihar da kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...